Sakamakon Zaɓuɓɓukan Abuja Da Ribas Ya Nuna Ƙarin Goyon Baya Da Ƴan Najeriya Ke Yi Wa Tinubu – A Cewar Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya bayyana cewa sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi na FCT da kuma zaɓen cike gurbi na jihar Rivers ya nuna yadda jama’a ke ƙara amincewa da manufofi da shirye-shiryen Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.

Wike ya faɗi haka ne a ranar Lahadi yayin da yake martani kan sakamakon zaɓukan, inda jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta samu gagarumar nasara.

Ya ce nasarar jam’iyyar, musamman a yankunan karkara na FCT, na nuna cewa shirye-shiryen gwamnati na fara yin tasiri ga rayuwar jama’a a matakin ƙasa.

A cewarsa, wannan shi ne karon farko da APC ta samu kujerun kansiloli a wasu yankuna na karkara, tare da samun rinjaye mai yawa a kujerun shugabannin ƙananan hukumomi.

Tsohon gwamnan na jihar Rivers ya kuma yi tsokaci kan sakamakon zaɓen cike gurbi a jihar, inda ya bayyana nasarar APC a matsayin ta haɗin gwiwar ‘yan siyasa daban-daban da ya kira “rainbow coalition”.

Ya ƙara da cewa wannan haɗin kai na nuna yadda bangarori daban-daban ke goyon bayan ajandar “Renewed Hope” ta Shugaba Tinubu.

More from this stream

Recomended