Attajirin Afirka, Aliko Dangote, ya dauki matakin bai wa iyalansa muhimmiyar rawa a tafiyar da harkokin Kamfanin Dangote Group, inda ya nada ’ya’yansa mata uku a manyan mukamai.
Wannan mataki na nuna sabon salo na mika ragamar shugabanci ga ’yan gida da kuma bai wa ƴan sabon zamani damar jagoranci.
Dangote, wanda rahoton Bloomberg Billionaires Index ya nuna cewa dukiyarsa ta kai dala biliyan 31.9, ya samu karin dala biliyan 1.89 a dukiyarsa cikin wannan shekara kadai.
An kuma ce yana samun karin kusan dala miliyan 50.8 a rana.
Babban ginshikin arzikin nasa, matatar mai ta Dangote wadda ita ce mafi girma a Afirka, ta fara aiki a farkon shekarar 2024.
Wannan ya kara bunkasa dukiyarsa tare da fadada manufofin kamfanin.
Aliko Dangote Ya Nada ’Ya’yansa Mata Uku A Manyan Mukamai A Kamfaninsa

