Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya naɗa gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, a matsayin Jakadan shirin Renewed Hope, kuma Mataimakin Darakta Janar mai kula da wayar da kai, hulɗa da jama’a da kuma tattara goyon baya ga jam’iyya.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Talata. Sanarwar ta ce naɗin ya fara aiki nan take.
Tinubu, wanda shi ne jagoran Jam’iyyar APC, ya bayyana cewa an zaɓi Uba Sani ne bisa “ƙwarewar jagoranci da kuma iya tsara al’amura” da yake da su.
Shugaban ƙasar ya ce gwamnan zai yi aiki kafaɗa da kafaɗa da Darakta Janar na shirin Renewed Hope da kuma manyan shugabannin jam’iyya, musamman shugaban APC na ƙasa, domin tabbatar da haɗin kai, haɗa kowa da kowa da kuma kyakkyawar daidaituwa a dukkan matakan wayar da kai da neman goyon baya.
Tinubu ya ƙara da cewa ana sa ran sabon naɗaɗɗen jami’in zai “tattara, yaɗa tare da bayyana manufofi da shirye-shiryen jam’iyya, ciki har da nasarori da ci gaban da aka samu,” domin ƙarfafa amincewar jama’a da kuma faɗaɗa saƙon Renewed Hope a faɗin ƙasar.
Shugaba Tinubu Ya Gwangwaje Uba Sani Da Sabon Muƙami

