Tinubu Ya Jinjina Wa Nuhu Ribadu, Ya Ce Za A Murƙushe ‘Yan Ta’adda

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta yi nasara a yaƙi da ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga da ke addabar al’ummar Najeriya.

Shugaban ya faɗi haka ne a ranar Litinin yayin da yake yabawa Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro, Nuhu Ribadu, bisa rawar da yake takawa wajen ƙarfafa tsaron ƙasa.

Tinubu ya bayyana Ribadu a matsayin mutum “mai gaskiya, jarumi, mai ƙarfin hali, kuma mai jajircewa a aikinsa.”

Yabon na zuwa ne a lokacin da shugaban ƙasar ya kai ziyara Jihar Adamawa State, inda ya nuna gamsuwa da jagoranci da ƙoƙarin Ribadu wajen inganta tsaro a faɗin ƙasar.

Haka kuma, Tinubu ya sake nanata ƙudirin Gwamnatin Tarayya na kawo ƙarshen matsalar tsaro a Najeriya, yana mai cewa ƙarƙashin jagorancin Ribadu, ƙasar za ta shawo kan ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda.

More from this stream

Recomended