Amurka za ta girke sojoji 200 a Najeriya

Kasar Amurka na shirin girke sojoji 200 a Najeriya nan da  yan makonni masu zuwa kamar yadda jaridar Wall Street Journal ta rawaito.

Wata majiya dake gwamnatin Amurka ta fadawa jaridar cewa za a tura sojojin ne sakamakon gazawar da gwamnatin Najeriya ta yi wajen yaki da yan ta’adda a kasar.

Majiyar ta bayyana cewa sojojin  za su taimaka ne wajen bayar da horo ga dakarun sojan Najeriya ba wai su shiga a fagen daga ba .

Wannan dai ƙari ne kan wata yar karamar tawagar sojan Amurka da tuntuni su ke Najeriya.


Sanarwar girke dakarun na zuwa ne dai-dai lokacin da ake cigaba da samu kyakkyawar alaƙa tsakanin Amurka da Najeriya a yaki da mayakan Boko Haram, ISWAP.

More from this stream

Recomended