Mayakan Boko 8 Sun Mika Wuya Ga Sojoji

Kwamanda rundunar tsaron haɗin gwiwa ta Operation Hadin Kai a yankin arewa maso yamma General I.S Ali ya ce mayakan Boko Haram 8 ne suka mika wuya ga rundunar a ranar Laraba.

Ali wanda ya bayyana haka lokacin da yake miƙa ragamar jagorancin rundunar ga Major General Gold Chibuisi ya ce kawo yanzu sama da yan ta’adda 100,000 ne tare da iyalinsu suka mika wuya ga rundunar a yankin arewa maso gabas.

“Jiya-jiyan nan (Laraba) 8 daga cikinsu suka zo tare da bindigoginsu.”

Ya kara da cewa rundunar a karkashin sa cikin watanni shida ta samu nasarar kai farmaki da dama ciki tare da kwato makamai a wuraren irin su Ukuba dake cikin dajin Sambisa.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]