An ba da belin Dr. Dutsen Tanshi

Wata kotun majistare a Bauchi ya bayar da belin wa Dr. Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi.

Hakan na zuwa ne bayan an tsare shi na wasu sa’o’i a gidan yari.

Lauyoyin Dr. Dutsen Tanshi dai sun faɗa cewa wanda suke ba wa kariya ya cancanci a ba shi beli saboda hakan bai saba wa dokar Najeriya ba.

Idan ba a manta ba, wata kungiya da ake kira Fityatul Muslim ita ta kai shunensa ga hukuma da zargin cewa ya faɗi munanan kalamai ga Manzon Allah (SAW), wanda shi kuwa a nasa bangaren ya musanta hakan.

More from this stream

Recomended