
Hakkin mallakar hoto
Getty Images
Hukumar kwallon kafa ta Afirka, CAF ta bayyana ‘yan kwallo uku da za a zabi gwarzon da babu kamarsa a 2019.
Cikin ukun da ta sanar sun hada da dan wasan tawagar Algeria da Manchester City, Riyad Mahrez da na Masar da Liverpool, Mohamed Salah da na Senegal da Liverpool, Sadio Mane.
Mane da Salah sun taimaka wa Liverpool ta lashe kofin Zakarun nahiyoyi, kuma Salah na takara karo na uku a jere.
Mahrez shi ne ya ja ragamar Aljeria ta lashe kofin nahiyar Afirka da aka yi a Masar, inda Mane ya taimaka wa Senegal zuwa wasan karshe a 2019.
Haka kuma an fitar da sunayen mata uku da za a zabi wadda babu kamarta a fagen kwallon kafar Afirka a shekarar nan.
Wadan da aka bayyana sun hada da Ajara Nchout ta tawagar Kamaru da kungiyar Valerenga da Asisat Oshoala ta Najeriya Barcelona da ‘yar wasan tawagar Afirka ta Kudu mai taka leda a Beijing Phoenix, Thembi Kgatlana.
Koci-Koci da daraktan tsare-tsare da kyaftin din mambobin tawagogin kwallon kafar Afirka ne za su yi zaben gwarzayen bana.
Za a bayyana wadan da suka yi fice a Afirka a wani biki da CAF za ta gudanar ranar 7 ga watan Janairu a otal mai suna Hurghada da ke Masar.
Dan kwallon da babu kamarsa a bana:
Macen da ta yi fice a tamaula a bana:
Dan wasan da ya yi kwazo a kungiyar Afirka a bana:
Matashin dan kwallon da babu kamarsa a Afirka a bana:
Kocin da babu kamarsa a bana:
Macen da ta fi yin fice a fagen koci a bana:
Tawagar kwallon kafa ta maza da ta fi yin bajinta a bana:
Tawagar kwallon kafa ta mata da babu kamarta a bana: