Tinubu Ya Gana Da Wasu Shugabannin Kasashen Afrika Ta Yamma

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da shugabannin wasu kasashen Africa ta yamma su uku a fadar Aso Rock dake Abuja.

Shugabannin su ne Patrice Tallon na Jamhuriyar Benin, Umaro Sissoco Embalo na Guinea-Bissau da kuma shugaban kasar Jamhuriyar Nijar, Muhammad Bazoum.

Shugabannin kasashen uku da suka isa fadar Aso Rock ɗaya bayan ɗaya sun samu tarba daga shugaban kasa, Tinubu a gaban ginin ofishinsa.

Duk da cewa babu wata ajenda da aka bayyana kan taron ana ganin ganawar ta su zata mayar da hankali kan batun tattalin arziki.

More from this stream

Recomended