Tinubu Ya Gana Da Wasu Shugabannin Kasashen Afrika Ta Yamma

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da shugabannin wasu kasashen Africa ta yamma su uku a fadar Aso Rock dake Abuja.

Shugabannin su ne Patrice Tallon na Jamhuriyar Benin, Umaro Sissoco Embalo na Guinea-Bissau da kuma shugaban kasar Jamhuriyar Nijar, Muhammad Bazoum.

Shugabannin kasashen uku da suka isa fadar Aso Rock ɗaya bayan ɗaya sun samu tarba daga shugaban kasa, Tinubu a gaban ginin ofishinsa.

Duk da cewa babu wata ajenda da aka bayyana kan taron ana ganin ganawar ta su zata mayar da hankali kan batun tattalin arziki.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]