‘Yan Banga Da Mafarauta Sun Sami Horon Cudanya Da Al’umma

A ci gaba da neman mafita ga matsalar tsaro a Nijeriya, Majalisar dinkin duniya, karkashin shirin taimakawa kasashe masu tasowa, ta horadda ‘yan kato da gora, ‘yan banga da mafarauta.

Majalisar ta koyar da su dabarun cudanya da al’umma da hada kai da jami’an tsaro, don samun mafita kan matsalar tsaro a Arewa maso gabashin Najeriya.

Matasa dari hudu ne daga jihohin Adamawa da Yobe, suka zo cibiyar koyar da dabarun shugabanci da zama dan kasa na gari a Jos jihar Filato.

An horar da su yadda zasu kaucewa take hakkin dan adam, fahimtar darajar al’adun al’umma da hadin kai wajen gudanar da aikinsu ba tare da nuna bambancin addini ko kabila ba.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]