‘Yan Banga Da Mafarauta Sun Sami Horon Cudanya Da Al’umma

A ci gaba da neman mafita ga matsalar tsaro a Nijeriya, Majalisar dinkin duniya, karkashin shirin taimakawa kasashe masu tasowa, ta horadda ‘yan kato da gora, ‘yan banga da mafarauta.

Majalisar ta koyar da su dabarun cudanya da al’umma da hada kai da jami’an tsaro, don samun mafita kan matsalar tsaro a Arewa maso gabashin Najeriya.

Matasa dari hudu ne daga jihohin Adamawa da Yobe, suka zo cibiyar koyar da dabarun shugabanci da zama dan kasa na gari a Jos jihar Filato.

An horar da su yadda zasu kaucewa take hakkin dan adam, fahimtar darajar al’adun al’umma da hadin kai wajen gudanar da aikinsu ba tare da nuna bambancin addini ko kabila ba.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]