Ƴan Sandan Kebbi Sun Musanta Jita-Jitar Rufe Makarantu Saboda Matsalar Tsaro


Rundunar ’yan sandan Jihar Kebbi ta musanta rahotannin da ke cewa an rufe makarantu a jihar saboda rashin tsaro, tana mai bayyana cewa labaran ba su da gaskiya.

Mai magana da yawun rundunar, SP Bashir Usman, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Birnin Kebbi, inda ya ce babu gaskiya a ikirarin da ke cewa an rufe makarantu ko kuma iyaye na cire ’ya’yansu daga makaranta saboda tsaro.

Ya ce ɗalibai sun koma makaranta domin sabon zangon karatu, yayin da masu kammala sakandare ke rubuta jarabawar kammala makaranta a cibiyoyi daban-daban cikin kwanciyar hankali.

Usman ya ƙara da cewa kalandar makarantu tana gudana karkashin kulawar Ma’aikatar Ilimi ba tare da wata tangarda daga matsalolin tsaro ba.

Ya kuma bayyana cewa hukumomin tsaro tare da haɗin gwiwar masu sa-kai na ci gaba da gudanar da ayyukan tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al’umma, tare da kira ga jama’a su yi watsi da jita-jitar da ka iya haifar da fargaba.

More from this stream

Recomended