Ƴan bindiga sun kashe likita a Nasarawa

Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba sun kashe Dr Stephen Angbas, mamallakin asibitin Lafia-Angbas.

Mummunan lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata a lokacin da Angbas ke kan hanyarsa ta zuwa gonarsa a kan babur da ke karamar hukumar Awe a jihar Nasarawa.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa maharan wadanda ake zargin ’yan fashi da makami ne, sun kai wa Angbas da wani ɗan Okada mai rakiyar sa hari.

Wani babban jami’i daga karamar hukumar, Mista Ibrahim ya nuna matukar damuwarsa kan lamarin.

Ya kuma nuna cewa shugaban ƙungiyarsu ya sanar da hukumomin tsaro domin su shiga lamarin cikin gaggawa.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...