Ziyarar Muhammadu Buhari a Maiduguri

Shugaban Najeriya Muhammdu Buhari na ziyarar a birnin Maiduguri da ke jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya, inda ya je domin halartar taron sojin kasar da ake yi a kowacce shekara.

Ziyarar ta Buhari na zuwa ne, a daidai lokacin da ake ci gaba da jimamin kisan wasu sojin kasar da ake zargin kungiyar Boko Haram da aikatawa a yankin Metele.

Rahotanni da dama sun ce sama da sojoji 100 aka kashe a wannan hari, ko da yake, rundunar sojin kasar ba ta fito ta fadi takamaiman adadin sojojin da ta rasa ba, duk da cewa ta tabbatar da aukuwar harin.

Wakilinmu Haruna Dauda Biu da ke Maiduguri ya ce Buhari ya fara ziyarar ce da kai gaisuwa a fadar Shehun Borno, Abubakar Ibn Umar Garba.

Sannan ya kai ziyarar asibiti domin yin jaje ga sojojin da suka samu raunuka a harin na Metele.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...