Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Juma’a a matsayin hutun ranar dimakwaradiya

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Juma’a a matsayin ranar hutu domin tunawa da ranar dimakwaradiya.

Olabunmi Tunji-Ojo ministan harkokin cikin gida ne ya sanar da haka a ranar Alhamis a cikin wata sanarwa da babbar sakatariyar ma’aikatar, Magdalene Ajani ta fitar.

” Ranar 12 ga Yuni za ta cigaba da  kasancewa mai muhimmanci a tarihin siyasar Najeriya domin girmama kwarin gwiwa, juriya da kuma sadaukarwar yan Najeriya waÉ—anda Æ™oÆ™arinsu ya tabbatar da mulkin dimakwaradiya a Æ™asar nan,” a cewar sanarwar.

Ministan ya kara da cewa ma’aikatarsa tare da sauran hukumomin tsaro za su cigaba da hada kai wajen samarwa ta re da karfafa matakan tsaro domin kare rayuka da dukiyar al’umma.

A shekarar 2018 ne tsohon shugaban kasa, Muhammad Buhari ya ayyana ranar 12 ga watan Yuni a matsayin ranar dimakwaradiya a maimakon ranar 29 ga watan Mayu.

Buhari ya É—auki matakin ne domin girmamawa tare da tunawa da Moshood Abiola.

More from this stream

Recomended