Zan rike Aubameyang komai rintsi—Arteta

Arsenal
Hakkin mallakar hoto
Getty Images

—BBC Hausa

Mikel Arteta ya ce Arsenal za ta rike Pierre-Emerick Aubameyang ko ta wane hali domin ya ci gaba da zama a Emirates.

Kocin na Arsenal ya ce za su zauna da dan wasan na tawagar Gabon kafin karshen kakar nan, domin tsawaita yarjejeniyar kyaftin din.
Kwantiragin Aubameyang zai kare ne a karshen kakar 2020-21.
Aubameyang, mai shekara 30, ya ci kwallo 20 a fafatawar da ya yi wa Gunners a bana, ana kuma cewa Barcelona da Inter Milan za su yi zawarcinsa.
Arteta ya ce ”Tabbas Arsenal za ta zauna da dan kwallon Gabon kan tsawaita zamansa a Gunners kan karshen kakar bana.
”Amma makomar tattaunawa da Aubameyang za ta ta’allaka kan kokarin Gunners a karshen kakar shekarar nan ”.
Arsenal tana mataki na 10 a kan teburin Premier da maki takwas tsakaninta da ta hudu Chelsea.
Arsenal ta fice daga gasar Zakarun Turai ta Europa League a karawar zagaye na biyu, bayan da Olympiakos ta yi nasara a kanta.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]