Za a ci gaba da wasannin neman shiga Gasar kofin Afirka

Afcon Qualifiers

Ranar Laraba za a ci gaba da wasannin neman gurbin shiga gasar Cin Kofin nahiyar Afirka da za a fafata a 2021.

Kimanin wasa 48 za a kara, inda tawagogin kasashen za su ci gaba da buga wasanni na uku- uku, wasu kuma na hur-hudu a cikin rukuni.

Wasu kasashen ma sun dauki sabbin masu horar da tamaula da suke sa ran za su kai su gasar da za a yi a Kamaru.

Tun farko bullar cutar korona ce ta dagula komai da tasa dole aka dakatar da wasannin aka kuma dage gasar kamar yadda aka tsara tun farko da za a yi cikin 2021.

Saura wasanni hur-hudu da suka rage don samun kasashe 24 da za su wakilci Afirka a gasar da za a buga, wacce za a yi a 2022.

Kawo yanzu ‘yan wasa uku ne ke kan gaba wajen cin kwallo a wasannin da suka hada da Victor Osimhen na Najeriya.

Sauran sun hada da Famara Diedhiou na Senegal da kuma Wahbi Khazrina Tunisia.

Algeria ce mai rike da kofi, wacce ta zama zakara a gasar da aka yi a Masar a 2019.

Wasannin da za a buga ranar Laraba 11 ga watan Nuwamba 2020:

  • Uganda da Sudan ta Kudu
  • Senegal da Guinea-Bissau
  • Kenya da Tsibirin Comoros
  • Mauritania da Burundi
  • Cape Verde da Rwanda
  • Libya da Equatorial Guinea

Ranar Alhamis 12 ga watan Nuwamba 2020:

  • Kamaru da Mozambique
  • Zambiada Botswana
  • Ghana da Sudan
  • Algeria da Zimbabwe
  • Ivory Coast da Madagascar
  • Burkina Faso da Malawi
  • Gabon da Gambia

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...