Daga ranar 18 ga watan Nuwamba ake fara yakin neman zaben shugaban kasa a Najeriya da ya ‘yan majalisar tarayya.
Za a kuma ci gaba da gudanar da yakin neman zaben har sai jajibirin ranar kada kuri’a.
Mai magana da yawun hukumar zabe INEC, Aliyu Bello ya shaidawa BBC cewa ‘yan takara za su shafe wata uku suna gangamin yakin neman zabe.
Ya kara da cewa har yanzu INEC tana kan matsayarta na duk wanda ya karya dokokin da aka gindaya to zai fuskanci hukunci.
Amfani da ‘yan bangar siyasa masu tada zaune tsaye, da kalaman batanci ko zagi na daga cikin abubuwan da hukumar zaben ta haramtawa ‘yan takara ko magoya bayansu aikatawa.
Fafatawa za ta fi zafi ne tsakanin shugaba Muhammadu Buhari na Jam’iyyar APC mai mulki, da Atiku Abubakar na babbar jam’iyyar hamayya ta PDP.