Zaɓaɓɓun Sanatoci Daga Arewa Sun Ce Dole Sai Shugaban Majalisar Dattawa Ya Fito Daga Yankin Su

Sanatocin da aka zaɓa daga yankin arewa sun dage cewa dole sai shugaban majalisar dattawa ya fito daga yankin arewacin kasarnan.

Wasu bayanai sun bayyana cewa zaɓaɓbun sanatocin 39 cikin 58 da suka fito daga jam’iyyu daban-daban sun gudanar da wani taro ranar Lahadi a Abuja inda suka cimma matsaya kan batun.

Wani sanata daga shiyar arewa maso yamma da yafi so kada a bayyana sunansa ya ce sanatoci da suka fito daga arewa sun dage sai shugaban majalisar dattawa ya fito daga yankin domin sakawa yankin kan goyon bayan takarar Bola Ahmad Tinubu a zaɓen da wuce.

Ya ce taron ya yanke matsayar tuntubar takwarorinsu da suka fito daga yankin kudu domin samun goyon bayansu.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]