Zaɓaɓɓun Sanatoci Daga Arewa Sun Ce Dole Sai Shugaban Majalisar Dattawa Ya Fito Daga Yankin Su

Sanatocin da aka zaɓa daga yankin arewa sun dage cewa dole sai shugaban majalisar dattawa ya fito daga yankin arewacin kasarnan.

Wasu bayanai sun bayyana cewa zaɓaɓbun sanatocin 39 cikin 58 da suka fito daga jam’iyyu daban-daban sun gudanar da wani taro ranar Lahadi a Abuja inda suka cimma matsaya kan batun.

Wani sanata daga shiyar arewa maso yamma da yafi so kada a bayyana sunansa ya ce sanatoci da suka fito daga arewa sun dage sai shugaban majalisar dattawa ya fito daga yankin domin sakawa yankin kan goyon bayan takarar Bola Ahmad Tinubu a zaɓen da wuce.

Ya ce taron ya yanke matsayar tuntubar takwarorinsu da suka fito daga yankin kudu domin samun goyon bayansu.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]