Yara Shida Da Aka Sace A Kaduna Sun Samu ’Yanci Bayan Kwanaki 36

Mutane tara da suka haɗa da yara shida masu zuwa makaranta, direbansu da wasu manya biyu sun samu ’yanci bayan sun shafe kwanaki 36 a hannun masu garkuwa da mutane a Jihar Kaduna.

An sace su ne a ranar 26 ga Afrilu, 2026, a kan titin Akwando zuwa Kachia lokacin da wasu ’yan bindiga suka kai hari kan motar da ke ɗaukar ɗalibai zuwa makaranta.

Kakakin Kuturmi Unity Development Association (KUDA), Mista Manasseh Samuel, ya tabbatar da sakin mutanen, inda ya ce sun dawo gida da safiyar Lahadi bayan sun yi tafiyar kusan sa’o’i shida a cikin daji.

Shi ma tsohon mai taimaka wa marigayi gwamnan Kaduna, Patrick Ibrahim Yakowa, kan harkokin yaɗa labarai, Reuben Buhari, ya tabbatar da faruwar lamarin tare da gode wa Allah da kuma waɗanda suka taimaka da addu’o’i da sauran gudummawa.

Buhari ya ce yaran sun fuskanci ƙalubale masu yawa a lokacin da suke tsare, lamarin da ya sa suka rasa kusan zango guda na karatu. Ya kuma yi kira da a ci gaba da yin addu’a domin sauran mutanen da har yanzu suke hannun masu garkuwa da mutane a ƙauyukan Awon da Ariko.

More from this stream

Recomended