‘Yan zanga-zanga sun hana zaman shari’ar Mu’azu Magaji a Kano

Masu zanga-zanga sun kawo wa zaman kotu cikas yayin da take ƙoƙarin ci gaba da sauraron ƙarar Mu’azu Magaji (Win Win) kan zargin cin zarafin Gwamna Ganduje da iyalansa.

Wakilin BBC a Kano ya ambato jami’an kotun da ke Nomans Land, Sabon Gari a Kano na cewa ba za su fara sauraron ƙarar ba har sai ‘yan zanga-zangar sun bar wurin.

Matasa ɗauke da kwalaye da ke nuna goyon baya ga tsohon kwamashinan na ayyuka sun yi cincirundo a bakin kotun, yayin da wasu ɗalibai kuma ke kiran da a hukunta shi.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]