‘Yan zanga-zanga sun hana zaman shari’ar Mu’azu Magaji a Kano

Masu zanga-zanga sun kawo wa zaman kotu cikas yayin da take ƙoƙarin ci gaba da sauraron ƙarar Mu’azu Magaji (Win Win) kan zargin cin zarafin Gwamna Ganduje da iyalansa.

Wakilin BBC a Kano ya ambato jami’an kotun da ke Nomans Land, Sabon Gari a Kano na cewa ba za su fara sauraron ƙarar ba har sai ‘yan zanga-zangar sun bar wurin.

Matasa ɗauke da kwalaye da ke nuna goyon baya ga tsohon kwamashinan na ayyuka sun yi cincirundo a bakin kotun, yayin da wasu ɗalibai kuma ke kiran da a hukunta shi.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]