
Yan takara gwamna shida ƙarƙashin jam’iyar APC daga jihar Yobe sun gana da mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima kan rikicin da ya biyo bayan fitar da ɗantakarar gwamna da aka yi gabanin zaɓen 2027.
Rukunin ƴan takarar da suka halarci ganawar sun haɗa da Hon. Muhammad Ibrahim Bomai, Sanata dake wakiltar mazaɓar Kudancin Yobe, Lawan Kolo Geidam, tsohon shugaban hukumar NEMA, Engr. Mustapha Maihaja.
Sauran sun haɗa da tsohon babban sifeta janar na ƴan sanda, Usman Alkali Baba, Kashim Musa Tumba da kuma Bashir Machina.
Jaridar Daily Trust ta bayyana cewa taron da ya gudana cikin sirri an yi shi ne a gidan mataimakin shugaban kasar dake Abuja dai-dai lokacin dake ake cigaba da cece-ku-ce tun bayan da aka fitar da sunan tsohon sakataren gwamnatin jihar, Baba Mallam Wali a matsayin wanda zai yiwa jam’iyar APC takarar gwamna a zaɓen 2027.
Taron ganawar ya mayar da hankali wajen lalubo hanyar da za a warware rikicin lami lafiya bisa amincewar kowa da kowa.
Mataimakin shugaban ƙasar ya shawarci mutanen da suka yi wa kansu laƙabi da G6 da su sake duba matsayar da su ka ɗauka ta adawar su da tsarin maslaha da aka bi wajen fitar da ɗantakarar kuma su rungumi tattaunawa domin samar da haɗin kai da zaman lafiya a jam’iyar.

