Yan shi’a sun yi zanga zanga kan harin da Isra’ila ta kai kan Cocin Saint Porphyrius dake Gaza

Mambobin kungiyar yan uwa musulmi ta Najeriya da aka fi sani da shi’a sun gudanar da zanga-zanga kan harin da dakarun sojan Isra’ila suka kai wani coci dake yankin zirin Gaza.

Kasar Isra’ila ta kai harin kan Cocin Saint Porphyrius inda mutane da dama suka mutu ciki har da mutanen da suka yi kaura daga gidajensu kuma cocin ta basu mafaka a harabarta.

Ofishin yaÉ—a labarai na Hamas dake Gaza ya ce FalasÉ—inawa kiristoci 18 ne suka mutu a harin.

Yan kungiyar ta shi’a sun gudanar da zanga-zangar ne a babban masallacin Juma’a na kasa dake Abuja bayan da aka idar da sallar Juma’a.

A wata sanarwa, Sheikh Sidi Munir Mainasara mamba a kungiyar ya nemi Æ´an Najeriya da su goyi bayan mutanen Gaza dake musgunawa.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...