Mambobin kungiyar yan uwa musulmi ta Najeriya da aka fi sani da shi’a sun gudanar da zanga-zanga kan harin da dakarun sojan Isra’ila suka kai wani coci dake yankin zirin Gaza.
Kasar Isra’ila ta kai harin kan Cocin Saint Porphyrius inda mutane da dama suka mutu ciki har da mutanen da suka yi kaura daga gidajensu kuma cocin ta basu mafaka a harabarta.
Ofishin yaÉ—a labarai na Hamas dake Gaza ya ce FalasÉ—inawa kiristoci 18 ne suka mutu a harin.
Yan kungiyar ta shi’a sun gudanar da zanga-zangar ne a babban masallacin Juma’a na kasa dake Abuja bayan da aka idar da sallar Juma’a.
A wata sanarwa, Sheikh Sidi Munir Mainasara mamba a kungiyar ya nemi Æ´an Najeriya da su goyi bayan mutanen Gaza dake musgunawa.