Yan sanda sun kama wani boka da sabuwar gawa da yake kokarin fafarɗo da ita

Rundunar yan sandan jihar Ogun ta ce jami’anta sun kama wani mai suna, Babatunde Kolawole mazaunin jihar wanda ake zargi da samun sabuwar gawa ta wani mutum Ado/Odo-Ota a karamar hukumar Ota ta jihar.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Omolola Odutola ita ta bayyana haka a cikin wata sanarwa.

Odutola ta ce jami’an kungiyar tsaro ta Amotekum ne suka fara kama mutumin kafin su mika shi ga hannun yan sanda.

Ta kara da cewa mutumin ya yi ikirarin cewa shi mai maganin gargajiya kuma ya na kokarin ya dawowa da mamacin ransa

Ta cigaba da cewa kawo yanzu an gaza gano inda mutumin ya samo gawar.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]