‘Yan Jarida Sun Samu Horo Kan Labaran Karya Da Kalaman Batanci

Masu fashin baki sun dade su na bayyana cewa labaran karya da na batanci sun zama ruwan dare a cikin al’umma, lamarin da ke sanya kiyayya a zukatan mutane ya kuma haifar da tashin-tashina. A ‘yan shekarun nan, an rasa rayuka da dukiyoyi masu dimbin yawa a Najeriya da ma wasu kasashen Afurka a bisa wannan dalili.

Wannan ya sa Cibiyar Fasahar Sadarwa Da Ci Gaban Jama’a wato Centre For Information Technology and Development (CITAD), tare da hadin gwiwar hukumar tallafa wa kasashe ta kasar Amurka, USAID, suka shirya wani taron bita ga yan jarida da kuma masu ruwa da tsaki a Jihar Adamawa don kauce wa rahotonnin da za su iya haifar da kiyayya, wato Hate Speech.

Masana da suka gabatar da makala a wajen taron, sun tabo batun illar yada rahotonin karya da kalaman batanci, kamar yadda wasu kafafen sadarwa ke yi, kana, cibiyar ta bayyana bukatar da ke akwai ga ‘yan jarida na hada hannu domin dakile wannan lamarin da ke kawo wa Najeriya ci baya.

Yada labaran karya a cikin al’umma musamman ma a kafafen sadarwa yana matukar sanya jamma’a cikin firgici da tashin hankali.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...