Dickson Ya Musanta Samun Rikici A Jam’iyyar NDC



Jagoran jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC), Sanata Seriake Dickson, ya ce babu wani rikici a cikin jam’iyyar duk da rade-radin da ake yi.

Dickson ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi a shirin Prime Time na tashar Arise Television a ranar Laraba.

Ya ce jam’iyyar na ci gaba da samun goyon baya daga fitattun ‘yan siyasa, ciki har da tsohon gwamnan Jihar Anambra, Peter Obi, da tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso.

A cewarsa, haɗuwar waɗannan jagorori a karkashin NDC wata alama ce ta amincewa da jam’iyyar, ba kuma alamar rikici ba.

Dickson ya gode wa ‘yan Najeriya kan amincewa da jam’iyyar, yana mai cewa yawan masu nuna sha’awar neman takara a karkashin NDC ya nuna irin karɓuwar da take samu a faɗin ƙasar.

More from this stream

Recomended