‘Yan Darikar Tijjaniyya sun gina katafaren masallaci a Amurka

Al’ummar Tijjanawa mazauna kasar Amurka, dake birnin New York, sun gina wani katafaren masallaci, da aka kashe miliyoyin dalolin kudade yayin aikin ginin sa.

Masallacin wanda aka yi wa lakabi da sunan babban Sahabin MANZON ALLAH (SAW) wato Sayyadi Abubakar, tuni ya soma jan hankalin al’ummar musulmin duniya, inda tuni musulmi dake fadin birnin New York suka soma hallara cikin sa domin yin ibada.

Al’ummar musulmi Tijjanawa dai sun shahara ne da zaman lafiya a duk inda suka kasance da duk al’ummar da suka kasance cikin ta, wanda hakan ya sanya wadanda ba musulmi ba ma basu shakkun rayuwa dasu.

Idan mai karatu bai manta ba, a makon da ya gabata ne al’ummar musulmi Tijjanawa suka bude wani katafaren masallaci da suka gina a kasar Sengal wanda ke daukar adadin masallata kusan dubu uku, masallacin da babu irin sa a fadin Afrika. Baya ga Gidauniyar ginin cibiyar Addinin Musulunci ta duniya da Sheikh Shariff Ibrahim Saleh ya yi assasa.

Allah Ya daukaka musulunci baki daya. Amiin

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...