‘Yan Boko Haram 2 Daga Chadi Sun Mika Wuya Ga Dakarun Najeriya | VOA Hausa

Wasu mayakan Boko haram ‘yan asalin kasar Chadi sun yi saranda tare da mika wuya ga dakarun sojojin Najeriya.

Abu Abor dan shekaru 61 da Abubakar Hassan dan shekaru 51, sun yi saranda ga dakarun sojin Najeriya na babban sansanin sojojin na goma sha daya dake Gamborun Ngala a jihar Borno.

Kanar Aminu Iliyasu, Mai Magana da yawun sashin aikace – aikace na hedikwatar sojin Najeriya, ya ce, binciken farko da suka gudanar ya tabbatar da cewa mayakan na bangaren shugaban Boko Haram, Abubakar Shekau, sannan suna zaune a wani matsuguni da suke kira Bagadaza, a zirin tafkin Chadi.

A ‘yan watannin da suka gabata sojojin Artillery na Najeriya suka ta kai munanan hare hare ga sansanonin ‘yan ta’addan, al’amarin da ya daidaita su tare da kassara su.

Abdullahi Aliyu Katsina, shugaban kungiyar samar da kyakkyawan shugabanci da tsaro a Nijeriya, ya yabawa sojojin Najeriya, sannan ya yi kira da cewa, ya kamata su dauki sabbin matakan yaki da kungiyar ta’addanci ta Boko Haram.

More News

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...