Yan bindiga sun yi garkuwa da wani jigo a jam’iyar APC

Yan bindiga sun yi garkuwa da Kawu Yakasai jami’in tsare-tsare na jam’iyar APC a jihar Kaduna.

An ce an yi awon gaba da Yakasai ne ranar Juma’a da daddare a karamar hukumar Soba ta jihar.

Kawo yanzu yan bindigar ba su bukaci a biya su kudin fansa ba ko kuma tuntubar iyalinsa.

Da yake ta tabbatar da faruwar lamarin ranar Asabar, Muhammed Shehu babban jami’in yada labarai na gwannan jihar Uba Sani ya ce tuni gwamnan ya bada umarnin jami’an tsaro su zakulo masu garkuwar su kuma kuɓutar da Yakasai.

Shehu ya ce gwamnatin jihar Kaduna na aiki domin daukar yan bijilante 7000 domin taimakawa kokarin da jami’an tsaro su ke yi.

More News

An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro. Mazaunan garin...

Sojoji sun ceto mutane 6 daga cikin ɗaliban jami’ar Gusau da aka sace

Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da...

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a. ‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun...

Ƴan sanda sun kama masu safarar makamai wa ƴan bindiga

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Karasuwa a jihar Yobe sun cafke wasu mutane biyu da ake zargi da kai wa ‘yan bindiga makamai da...