‘Yan bindiga sun sace ɗaliban kwaleji mata a Jihar Zamfara

‘Yan bindiga sun sace ɗaliban Kwalejin Kimiyyar Kiwon Lafiya mata huɗu ranar Talata da dare a Jihar Zamfara da ke arewacin Najeriya.

Wani mazaunin yankin ya faɗa wa BBC cewa maharan sun afka wa gidan da ɗaliban ke zaune wanda ke wajen makarantar a garin Tsafe bayan sun tarar da jami’an tsaro na gadin kwalejin.

Shugagan kwalejin, Yusuf Idris Maradun, ya ce ɗalibai biyar ‘yan bindigar suka kama amma daga baya suka saki ɗaya daga cikinsu saboda ta kasa tafiya sakamakon lalurar ƙafa.

Rundunar ‘yan sanda a jihar ta ce jami’an tsaro sun duƙufa domin ganin an ceto ɗaliban da aka sace a gidan da suka kama haya suna kwana a cikin garin na Tsafe.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]