Yan bindiga sun kashe mutum 4 tare da sace wasu mutane 18 a Sokoto

A ƙalla mutane huɗu aka kashe bayan da wasu da ake zargin yan bindiga ne suka kai hari kan kauyen Giyawa dake karamar hukumar Goronyo ta jihar Sokoto.

A cewar Ahmad Rufa’i mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar maharan sun kuma yi awon gaba da wasu mutane 18.

Rufa’i ya kara da cewa 7 daga cikin mutanen da aka sace sun kubuta inda suka dawo kauyen.

Ya kuma kara da cewa jami’in tsaro na bin sawun yan bindigar.

Jihar ta Sokoto na daga cikin jihohin da suke yankin arewa maso yamma dake fama da hare-haren yan bindiga.

More News

An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro. Mazaunan garin...

Sojoji sun ceto mutane 6 daga cikin ɗaliban jami’ar Gusau da aka sace

Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da...

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a. ‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun...

Ƴan sanda sun kama masu safarar makamai wa ƴan bindiga

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Karasuwa a jihar Yobe sun cafke wasu mutane biyu da ake zargi da kai wa ‘yan bindiga makamai da...