Yan bindiga sun kashe mutane 18 a jihar Filato

Aƙalla mutane 18 aka kashe a wasu hare-hare daban-daban da yan bindiga su ka kai kan kauyukan Kawel da Kopkon dake gundumar Mushere a karamar hukumar Bokkos ta jihar Filato.

Majiyoyin jami’an tsaro sun faɗawa kafar labarai ta Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi dama Najeriya baki da cewa sojojin shiya ta 5 dake aiki karkashin rundunar Operation Enduring Peace sun mayar da martani kan tsararren farmaki da yan bindigar su ka kai da karfe 1:24 na daren ranar 20 ga watan Yuni.

Majiyoyin sun bayyana cewa maharan sun farma ƙauyukan Kawel da Kopkon inda suka riƙa harbin kan me uwa da wabi kafin su tsere a yayin da jami’an tsaro ke ƙarasawa wurin.

Da isar jami’an tsaron sun gano gawar mutane 12 a ƙauyen Kawel a yayin da suka samu gawarwakin mutane shida a ƙauyen Kopkon.

Majiyar ta ce jami’an tsaron sun ƙaddamar da farmaki a baki ɗayan yankin domin  bin diddigi tare da kamo maharan da su ka tsere.

More from this stream

Recomended