Yan bindiga sun kai hari gidan tsohon minista Labaran Maku

Wasu yan bindiga da kawo yanzu ba a san ko suwaye ba sun kai farmaki gidan tsohon minista, Labaran Maku dake Akpata a karamar hukumar Nassarawa-Eggon ta jihar Nasarawa.

Maharan sun jikkata jami’an tsaro biyu a harin.

Daya daga cikin jami’an tsaron da suka samu rauni a harin ya fadawa yan jarida ranar Lahadi cewa yan bindigar sun kai farmaki gidan da misalin karfe 07:50 na dare.

“Batagarin sun kutso kai cikin gidan inda suka rika harbin kan me uwa da wabi har ta kai sun jikkata mutum uku daga cikinmu.” ya ce.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...