Wasu ‘Yan Bindiga A Zamfara Sun Karbi Da’awar Sheik Gumi Sun Ajiye Makamansu – AREWA News


Gawurtaccen ‘dan bindiga mai garkuwa da mutane a jihar Zamfara Auwalun Daudawa tare da yaransa sun karbi da’awar Dr Ahmad Gumi sun ajiye makamansu na ta’addanci.
Auwalun Daudawa ya rungumi zaman lafiya, ya mika makamansa na yaki, ya mikawa rundinar ‘yan sanda bindigogi kirar AK47 guda 20 da sauran manyan bindigogi da harsashi da wasu miyagun makamai.
Bayan haka, yayi rantsuwa da Qur’ani shi da yaransa cewa har abada ba zasu sake komawa ga mugun halinsu na baya ba.
Auwalun Daudawa yana daya daga cikin manyan kungiyoyin ‘yan bindiga da suka sace daliban makarantar Kankara.
Muna rokon Allah Ya karbi tubansu, Ya shiryar da sauran barayin, Ya sakawa Dr Ahmad Gumi da gidan Aljanna. Amin.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...