Trump Ya Sanar Da Tsagaita Wuta Tsakanin Lebanon Da Isra’ila

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa ƙasashen Lebanon da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta na kwanaki 10, wanda zai fara aiki da ƙarfe 5:00 na yamma agogon ƙasar.

A cikin wani saƙo da ya wallafa, Trump ya ce ya yi tattaunawa da shugaban Lebanon Joseph Aoun da kuma firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, inda suka cimma matsayar dakatar da rikicin na wucin gadi.

Sai dai bai bayar da cikakken bayani ba dangane da rawar da ƙungiyar Hizbullah ke takawa, wadda ke samun goyon bayan Iran a Lebanon, kuma tana musayar wuta da Isra’ila.

Trump ya ce: “Na tattauna da Shugaban Kasar Lebanon Joseph Aoun cikin girmamawa, da Firaminista Bibi Netanyahu na Isra’ila.

“Shugabannin biyu sun amince cewa domin a samu zaman lafiya a tsakanin kasashensu, za su fara tsagaita wuta na kwanaki 10 a hukumance da karfe 5 na yamma,” in ji Trump.

More from this stream

Recomended