Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake sukar ƙungiyar tsaro ta NATO, inda ya gargaɗe ta da ta nisanci mashigar Hormuz.
Wannan na zuwa ne bayan Faransa da Birtaniya sun sanar a ranar Juma’a cewa sun jagoranci wata rundunar ƙasashe da dama domin tabbatar da ƴancin zirga-zirgar jiragen ruwa a yankin.
Sai dai a wani saƙo da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Mista Trump ya yi watsi da duk wani yunƙurin taimako daga ƙasashen ƙungiyar, yana mai jaddada cewa kada jiragensu su kusanci mashigar.
Tun da farko, Trump ya sha sukar ƙasashen NATO, yana zarginsu da rashin cikakken goyon baya ga Amurka, musamman a rikicin da ta yi da Iran.
Trump Ya Sake Caccakar NATO Kan Batun Mashigar Hormuz

