Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu zai bar Abuja zuwa Lagos ranar Lahadi gabanin bikin ƙaramar sallah.
Mai magana da yawun shugaban Æ™asar, Ajuri Ngelale ya ce Tinubu zai yi amfani da lokacin tare da iyalinsa wajen yiwa Najeriya addu’a.
Ngelale ya ce shugaban ƙasar zai cigaba da gudanar da ayyukansa daga Lagos a lokaci da kuma bayan hutun sallah.
A ranar Litinin ne za a fara duban watan Shawwal b bayan da watan Azumin Ramadan ya cika kwanaki 29.