
Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya sauke Wale Edun daga mukaminsa na ministan kuɗi inda ya maye gurbinsa da Taiwo Oyedele wanda shi ne karamin ministan kudi.
A wata sanarwa da aka fitar ranar Talata, Yomi Odunuga mai bawa sakataren gwamnatin tarayya shawara kan kafafen yaɗa labarai ya bayyana cewa nan da zuwa ranar Alhamis ministan zai kammala mika aiki.
Har ila yau shugaban kasa ya sauke ministan gidaje, Architect Ahmed Musa Dangiwa daga mukaminsa na ministan gidaje da raya birane.
Shugaban ƙasar ya kuma fitar da sunan, Muntaka Rabe Darma a matsayin wanda zai zama sabon ministan gidaje da raya birane

