Tinubu ya rantsar da Akume a matsayin sakataren gwamnati

Shugaba Bola Tinubu ya rantsar da Sanata George Akume a matsayin sabon sakataren gwamnatin tarayya.

A ranar Laraba ne aka rantsar da Akume a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Akume, wanda tsohon Ministan Harkokin Cikin Gida ne, ya yi rantsuwar mubaya’a tare da rantsar da shi da misalin karfe 11:06 na safe a zauren majalisar da ke fadar Shugaban Ƙasa.

Taron ya samu halartar wasu daga cikin masu rike da madafun iko kuma tsofaffin gwamnoni da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima da shugaban majalisar dattawa Ahmed Lawan.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...