Shugaba Bola Tinubu ya rantsar da Sanata George Akume a matsayin sabon sakataren gwamnatin tarayya.
A ranar Laraba ne aka rantsar da Akume a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Akume, wanda tsohon Ministan Harkokin Cikin Gida ne, ya yi rantsuwar mubaya’a tare da rantsar da shi da misalin karfe 11:06 na safe a zauren majalisar da ke fadar Shugaban Ƙasa.
Taron ya samu halartar wasu daga cikin masu rike da madafun iko kuma tsofaffin gwamnoni da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima da shugaban majalisar dattawa Ahmed Lawan.