

Bayan shafe tsawon lokuta ana jiran tsammani a karshe majalisar dattawa ta sanar da sunayen da shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya mika mata domin tantancewa.
Tsofaffin gwamnoni, Nasiru Elrufai, David Umahi da kuma Nyesom Wike na daga cikin jerin sunayen mutanen da Tinubu zai naɗa ministoci.
Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio shi ne ya karanto sunayen a yayin zaman majalisar na ranar Alhamis.
Ga jerin sunayen nan a kasa: