Bola Ahmad Tinubu, tsohon gwamnan jihar Lagos kuma dantakarar shugaban kasa a jam’iyar APC ya godewa shugaban kasa, Muhammad Buhari saboda goyon baya da karfafa gwiwa da yake bashi.
Har ila yau Tinubu ya godewa Mai Martaba Sarkin Daura bisa addu’a da yake masa.
Tinubu ya bayyana haka ne cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter.
A ranar Lahadi ne dan takarar shugaban kasar ya ziyarci shugaban kasa, Muhammad Buhari a gidansa dake Daura.
![](https://arewa.ng/storage/screenshot_20220711_1133242758322451957273529.jpg)
![](https://arewa.ng/storage/screenshot_20220711_1132114494191105311543382.jpg)
![](https://arewa.ng/storage/screenshot_20220711_1133453691860254809607840.jpg)
![](https://arewa.ng/storage/screenshot_20220711_1131242493194658606601122.jpg)