Shugaban kasa Bola Tinubu ya gana da tsohon Sarkin Kano Sanusi Lamido Sanusi a ranar Alhamis.
Tinubu ya gana da Sanusin ne a fadar shugaban kasa a ranar Alhamis.
Da misalin karfe 5 na yamma ne tsohon gwamnan babban bankin Najeriya CBN ya isa fadar shugaban kasar domin ganawa da Tinubu, har yanzu ba a bayyana ajanda a taron ba.
Ziyarar ta Sanusi ta zo ne bayan da Tinubu ya dakatar da tsohon Gwamnan babban bankin Najeriya Godwin Emefiele.
Tinubu da Sanusi suna ganawa a karon farko tun bayan da ya dare kujerar shugaban kasa a ranar 29 ga watan Mayu.