Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dakatar da Gwamnan Babban Bankin Najeriya CBN, Godwin Emefiele.
Ofishin sakataren gwamnatin tarayya shi ne ya fitar da sanarwar dakatarwar.
Willie Bassey daraktan yaÉ—a labarai a ofishin sakataren gwamnatin tarayyar shi ne ya sanar da haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.
Sanarwar ta ce dakatarwar ta fara aiki nan take.