Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ɗaukar sabbin masu gadin daji dubu ɗaya a jihar Oyo, tare da kafa wata tawagar ceto ta musamman domin ƙarfafa tsaro a yankin, bayan garkuwa da ɗalibai da malamai a ranar goma sha biyar ga watan Mayu, shekara ta dubu biyu da ashirin da shida.
Matakin na zuwa ne bayan wata babbar tawagar gwamnatin tarayya ta kai ziyara ƙauyukan Esiele da Yawota da ke ƙaramar hukumar Oriire, domin duba halin da ake ciki tare da tattaunawa da shugabannin al’umma kan lamarin.
Tawagar, wadda ta ƙunshi manyan jami’an tsaro da gwamnati ciki har da Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, Mai ba Shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, da Sufeto-Janar na ‘Yan sanda, ta kuma bayyana cewa bukatar kafa sansanin soji a yankin za a kai ga Shugaban ƙasa domin nazari.
Haka kuma, an umurci rundunar ceto ta musamman mai amfani da bayanan sirri wajen ƙara ƙaimi domin ganin an ceto ɗaliban da malamai da aka sace cikin gaggawa.
Tawagar ta kuma ziyarci fadar Soun na Ogbomosho, inda ta jajanta masa da al’ummarsa, tare da gana wa da iyalan malamar da ta rasu a harin, tare da tabbatar musu da goyon bayan gwamnati.
Gwamnatin tarayya ta ce za a ci gaba da gudanar da aikin ceto cikin tsari na sirri da haɗin gwiwar matakan soji da na bayan fage domin tabbatar da ganin an dawo da waɗanda aka sace lafiya.
Tinubu Ya Amince Da Tura Masu Tsaron Daji 1000 Da Tawagar Ceto Ta Musamman a Oyo Bayan Sace Ɗalibai

