Sojojin Najeriya sun ce sun kashe ‘yan ta’adda 37 da ‘yan fashi 12

Dakarun rundunar Operation Hadin Kai ta sojojin Najeriya sun kashe mutanen da suka kira ‘yan ta’adda 37 a yankin arewa maso gabashin Æ™asar tare da kama wasu 17 cikin mako biyu da suka wuce.

Kazalika, dakarun sun kashe ‘yan fashin daji 12 sannan sun kama 15 tare da Æ™wace makamai 21 da Æ™unshin harsasai 117 iri daban-daban, ciki har da mota mai bindiga huÉ—u daga hannun mutanen.

Daraktan yaÉ—a labarai na rundunar sojin Najeriya, Manjo Janar Benard Onyeuko, shi ne ya bayyana hakan yayin jawabinsa game da ayyukan rundunar a mako biyu da suka wuce a Abuja ranar Alhamis.

Ya ce sun yi nasarar ceto mutum 16 da aka yi garkuwa da su, yayin da “Æ´an ta’adda” 863 da iyalansu suka miÆ™a wuya.

“Dakarunmu sun ci gaba da kai hare-hare kan ‘yan ta’adda da ‘yan fashin daji da sauran miyagu a dukkan sansanoni da ke faÉ—in Æ™asa cikin mako biyu da suka wuce, inda muka samu kyakkyawan sakamako,” in ji shi.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Wani mutumi ya kashe mahaifiyarsa a kan kudi

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun kama wani mazaunin kauyen Kajola da ke kusa da Apomu a jihar mai suna Lukman Adejoju bisa...

Mayaƙan Boko Haram Biyu Sun Miƙa Kansu Ga Sojoji

Rundunar dakarun soja ta ƙasa da ƙasa wato Multi National Task Force(MNJTF) a turance shiya ta 3 dake Monguno a Najeriya ta bayar da...

Sojoji a birnin Ibadan  sun kama Æ´an fafutukar kafa Æ™asar Oduduwa

Dakarun rundunar sojan Najeriya  sun samu nasarar kama wasu mutane masu fafutukar kafa ƙasar Oduduwa a birnin Ibadan na jihar Oyo. Masu fafutukar sanye da...