Sojojin Najeriya Sun Binne Janar Braimah Da Wasu Sojoji Da Aka Kqshe A Borno

Rundunar sojin Najeriya ta sanar da binne Birgediya Janar Omo Braimah tare da wasu sojoji da suka rasa rayukansu a wani hari da mayaƙan Boko Haram suka kai a jihar Borno.

Marigayin, wanda ya kasance kwamandan rundunar 29 Joint Task Force Brigade ƙarƙashin Operation Hadin Kai, ya mutu ne bayan harin da ‘yan ta’addan suka kai sansaninsu da ke Benisheikh a ƙaramar hukumar Kaga.

A wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na Facebook, ta ce an gudanar da jana’izar ne a ranar Laraba 15 ga watan Afrilu a barikin Maimalari da ke Maiduguri, babban birnin jihar.

An yi jana’izar ne a gaban iyalai, abokan aiki da sauran jama’a, inda manyan jami’ai suka halarta ciki har da gwamnan Borno Babagana Umara Zulum, Ministan Tsaro Christopher Musa, da babban hafsan sojin ƙasa tare da wasu manyan baki.

Rundunar ta bayyana marigayin da sauran sojojin a matsayin jarumai da suka sadaukar da rayuwarsu wajen kare ƙasar.

More from this stream

Recomended