Sojoji sun kubutar da yan mata 12 daga hannun mayakan ISWAP a jahar Borno

Dakarun sojan rundunar Operation Hadin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin  arewa maso gabashin Najeriya sun samu nasarar ceto wasu  yan mata 12  da mayakan kungiyar ISWAP su ka yi garkuwa da su daga gundumar Mussa a karamar hukumar Askira Uba ta jihar Borno.

Yan ta’addan sun yi awon gaba da yan matan ne a ranar 23 ga watan Nuwamba lokacin da suke girbin  amfanin gona a gonar su.

Harin da mayakan na ISWAP suka kai gundumar ya saka mazaunanta da yawa tserewa ya zuwa garuruwan dake kusa.

Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi ya ce an kubutar da yan matan ne s wani farmaki da dakarun sojan suka kai a ranar Asabar kamar yadda wasu majiyoyin jami’an tsaro suka sheda masa.

Yan mata da aka kubutar sun hada da The Fatima Shaibu ( shekaru 17), Fatima Umaru ( shekaru 15), Hauwa Abubakar (shekaru 18), Saliha Muhammed (shekaru 15), Sadiya Umaru (shekaru 17), Amira Babel (shekaru 15), Zara Adamu (shekaru 17), Nana Shaibu (shekaru 15), Zainab Musa (shekaru 18), Zainab Muhammed (shekaru 17), Jamila Saidu (shekaru 15) da kuma Hauwa Hamidu (shekaru 17).

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]