Sojoji sun kuɓutar da mata 15 da ƙananan yara daga hannun Boko Haram

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun kuɓutar da wasu mata 15 da kuma kananan yara da mayakan Boko Haram su ka yi garkuwa da su a jihar Borno.

A wata sanarwa da aka fitar ranar Laraba, Sani Uba jami’in yaɗa labarai na hedkwatar rundunar haɗin gwiwa ta Operation Haɗin Kai a yankin arewa maso gabas ya ce an samu nasarar kuɓutar da mutanen ne a lokacin da dakarun sojan su ke aikin nema da ceto mutane a yankin tsaunukan Mandara dake jihar Borno.

Uba ya ce mayakan na Boko Haram sun rika harba bama-bamai amma ba a samu asarar rayuka ba ko kuma ta kayan aiki daga ɓangaren dakarun sojan.

Ya kara da cewa dakarun sojan sun samu nasarar dakile wasu hare-hare da yan ta’addar suka tsara kai wa a garuruwan Kanama, Ngoshe da kuma Banki.

More from this stream

Recomended