
Dakarun rundunar sojan Najeriya sun kuɓutar da wasu mata 15 da kuma kananan yara da mayakan Boko Haram su ka yi garkuwa da su a jihar Borno.
A wata sanarwa da aka fitar ranar Laraba, Sani Uba jami’in yaɗa labarai na hedkwatar rundunar haɗin gwiwa ta Operation Haɗin Kai a yankin arewa maso gabas ya ce an samu nasarar kuɓutar da mutanen ne a lokacin da dakarun sojan su ke aikin nema da ceto mutane a yankin tsaunukan Mandara dake jihar Borno.
Uba ya ce mayakan na Boko Haram sun rika harba bama-bamai amma ba a samu asarar rayuka ba ko kuma ta kayan aiki daga ɓangaren dakarun sojan.
Ya kara da cewa dakarun sojan sun samu nasarar dakile wasu hare-hare da yan ta’addar suka tsara kai wa a garuruwan Kanama, Ngoshe da kuma Banki.

