Sojojin rundunar Operation HADIN KAI a Arewa maso Gabas sun kashe akalla ‘yan ta’adda 24 bayan wani artabu mai tsanani da ya faru a yankin Kukareta.
Rahotanni sun nuna cewa ‘yan ta’addan sun kai hari ne da tsakar dare, amma sojojin sun dakile harin cikin gaggawa tare da tilasta musu ja da baya.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar, Laftanar Kanal Sani Uba, ya ce sojojin sun yi nasarar dakile harin tare da jawo babbar asara ga maharan.
A yayin artabun, sojojin sun kwato makamai da alburusai masu yawa daga hannun ‘yan ta’addan. Sai dai sojoji biyu sun samu raunuka, yayin da wata tankar yaki ta samu matsala.
Rundunar ta ce ana ci gaba da bin sawun ‘yan ta’addan da suka tsere, tare da kudurin ci gaba da kai hare-hare domin murkushe su gaba daya.
Sojoji Sun Kqshe ‘Yan Ta’adda 24 A Artabu A Kukareta

