Zaratan sojojin sun yi arba da yan ta’addar inda suka samu nasarar kashe biyu daga ciki.
A wata sanarwa da rundunar sojan Najeriya ta wallafa a shafinta na Facebook ta ce sojojin sun kuma samu nasarar ceto wasu mata 6 da kuma yara goma wadanda yan ta’addar ke tsare da su.
Har ila yau rundunar ta samu nasarar gano wasu kayayyakin amfanin gona da yan BH suka sace inda kuma aka kona su nan take a wurin.
Ga wasu daga cikin hotunan abinda ya faru:






